Duniya Labari

Duniya Labari

Share

Dan jarida Mai zaman khansa chikekken suna abdulkareem salisu abdulkareem

19/06/2026

To fa waye wannan kuma????

19/06/2026

Mace Ta Bayyana Azabar Da Ta Sha A Hannun ’Yan Bindiga, Ta Ce An Tilasta Mata Binne ’Ya’yanta Uku A Daji

Wata mata mai suna Aisha ta bayyana irin mawuyacin halin da ta tsinci kanta a ciki bayan ta fada hannun masu garkuwa da mutane a jihar Zamfara, inda ta ce an tilasta mata binne ’ya’yanta uku da s**a rasu yayin da suke tsare a cikin daji.

A cewar matar, rayuwar da s**a yi a hannun masu garkuwa da mutanen ta kasance cike da wahala, yunwa da rashin kulawa, lamarin da ya jefa iyalinta cikin matsananciyar ƙunci. Ta ce rasuwar yaran nata ta kasance daya daga cikin mafi munin abubuwan da ta taba fuskanta a rayuwarta.

Ta bayyana cewa bayan mutuwar yaran, an tilasta mata da kanta ta binne su a cikin daji ba tare da samun taimako ko damar kai su gida domin yi musu jana’iza yadda ya kamata ba.

Lamarin ya sake haskaka irin bala’in da matsalar garkuwa da mutane da ayyukan ’yan bindiga ke haifarwa ga al’ummomin da ke zaune a yankunan da matsalar tsaro ta fi kamari, musamman a Arewa maso Yammacin Najeriya.

Masu rajin kare haƙƙin ɗan Adam da masu sharhi kan harkokin tsaro na ci gaba da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da ceto waɗanda ke hannun masu garkuwa da mutane.

Labarai masu sahihanci, inganci da zurfin bincike daga Najeriya da duniya.

19/06/2026

Sojojin Nijar sun yi karon-batta da 'yan ta'adda, sun kashe 22, sun rasa sojojinsu 11

https://hausa.premiumtimesng.com/rahotanni/86812-sojojin-nijar-sun-yi-karon-batta-da-yan-taadda-sun-kashe-22-sun-rasa-sojojinsu-11.html

19/06/2026

Mawaki Dauda Kahutu Rarara Kenan a Yayin da Yake Sauraron Karatun Alkur'ani Mai girma Kuma Yake rubutawa a Jikin Allo.

19/06/2026
19/06/2026

Auta Waziri fitaccen mawakin Hausa ne daga jihar Kaduna. Sunansa na ainihi Abdullahi Abubakar, kuma ya shahara wajen rera wakokin soyayya da na al'adun Hausawa.

Asali
Ya fito daga Jihar Kaduna, Najeriya.
Ya yi karatun firamare da sakandare a Kaduna.

Sana'a
Ya fara yin waka tun yana matashi.
Ya yi fice da wakoki kamar:
Yar Budurwa
Lokaci
Ga Labarina
Zuciya
Aljannata

Aure
Auta Waziri ya yi aure da Halima Mustapha a watan Disambar 2024 a Kaduna.

Shekaru
Rahotanni sun nuna an haife shi ne a shekarun 1990s, amma ba a bayyana takamaiman ranar haihuwarsa a fili ba. Ana kiyasta yana cikin shekaru 30 zuwa sama da haka.

Kamfanin waka
Shi ne shugaban Diamond Star Music, kuma yana da dimbin masoya a Arewacin Najeriya.

Auta Waziri (Abdullahi Abubakar) mawaki ne daga Jihar Kaduna, kuma ya yi fice da wakoki kamar Yar Budurwa, Ga Labarina, Lokaci, da Kewa. Rahotanni sun nuna cewa yana cikin shekaru 30 zuwa sama kuma ya yi aure a shekarar 2024.

19/06/2026

To yan gidan Sarauniyar ingila shugabannin iya turanci, sai ku fadan rashin iya turanci da me ya rage mijina

Kuma Masu cewa mijina bai iya turanci ba sun manta dama shi bahaushe ne, kuma sarkin wakar hausa.

Inji Aisha Humaira

19/06/2026

Hassana Ibrahim Rano daya daga cikin jaruman da ayyukansu suke magana a madadinsu. saboda yadda ake ganin tana kara samun gurbi a masana'antar a hankali.

Ta fara jan hankalin masoya fina-finan Hausa ta hanyar fitowa a fina-finai da dama tare jan ragamar shiri mai dogon zango Zabi Biyu, rawan da ta taka ta nuna cewa tana da burin zama daya daga cikin fitattun jarumai a masana'antar.

Masu bibiyar Kannywood suna ganin tana daga cikin sabbin fuskokin da ke kokarin gina suna ba tare da hayaniya ba. akwai masu ganin Hassana na cikin wadanda ke da damar yin nisa idan ta ci gaba da irin wannan kokari.

Ko da yake har yanzu tana cikin matakin da ya kamata ta kara nuna cikakkiyar basirarta, domin akwai alamun da ke nuna cewa tana da abin da za ta bayar a gaba.

Shin Hassana Ibrahim Rano tana daga cikin sabbin jaruman Kannywood da za su iya zama manyan taurari nan gaba, ko har yanzu tana bukatar wasu manyan fina-finai kafin ta tabbatar da kanta?

19/06/2026

Rarara Ba Jahili Ba Ne masanin qur'anine, Kuma Yana Magana Ne Akan Gaskiya, Inji Fati Mohammed

19/06/2026

Mahaifiyarta ta shaidawa duniya cewa suna zargin dukanta da bulala tare da tsugunar da ita tsawon lokaci shi ne sanadiyar mutuwarta.

Korafin da iyayen mamaciyar s**a shigar gaban ‘yan sanda ya sanya kaddamar da bincike don gano musabbabin mutuwar ta Nihal.

Want your public figure to be the top-listed Public Figure in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Telephone

Website

Address

Dalah
Kano