Thabit Muhammad Ala
The mission of this channel is to convey the message of Islam to all the people around the globe.
Martanin Sheikh pantami zuwaga masu zaginsa.
02/07/2026
Ya allah kasa kar mushiga wannan gidan da hakkin wani akan mu🤲
23/04/2026
Wanann 1k Kuwaiti Dinar daidai take da naira miliyan 4 da dubu ɗari 3 😂😂
13/04/2026
Ma sha Allah. Muna taya Sheikh Bashir Aliyu Umar murna da samun promotion na matsayin Professor a Department na Islamic Studies, Bayero University, Kano (BUK).
Muna addu'a Allah ya sa albarka a wannan matsayi da ya samu. Allah ubangiji ya sa al'ummar Musulmai su ci gaba da amfana da ilimi da muqamin Sheikh Professor Bashir Aliyu Umar,. Ameen.
Duk wanda ya zagi manzon Allah tsakaninmu dashi kisa ne kawai....
Wannan itace aƙidarmu harmu koma ga Allah.
Idan Allah ya yika a Najeriya so yake ya jarrabeka..
03/04/2026
•'Yan uwa don Allah ku ƙara saka malamin Sunnah Sheikh Abdulrazak Yahya Haifan a Addu'a har yanzu yana jin jiki.
Allah ya bashi lafiya yasa kaffara ne Ameen.
Asalin Jos Garin Musulmi ne,
Saurara kaji yadda akayi....
02/04/2026
SAKAMAKON CIN NAMAN MUTANE
Al Imam Junaidul Baghdadi (rah) yace:
"Watarana ina tsaye a masallaci tare da jama'a masu yawa muna jiran isowar wata sallar janazah da za'a kawo, chan sai na hangi wani Almajiri, Faqiri, sufi (irin masu gudun duniyar nan).
Da ka kalleshi zaka ga alamar yawan ibadah atare dashi... Yana barar abincin da zai ci awajen mutane.
Sai na fa'da (acikin raina) "Yanzu wannan mai zai hana yaje yayi wani aikin da zai rika ciyar da kansa, ai da yafi masa".
Bayan na juya zuwa gidana, alhali ina da wasu ayyukan ibadah irin na yau da kullum da nake son yi, amma hakan bai yiwu ba. Kuma barci ya gagareni.
Chan cikin dare da barci ya daukeni sai nayi mafarki. Naga wannan mutumin ya zama gawa, an kwantar dashi agabana akan tebur, aka ce mun "GASHI NAN CI NAMANSA, TUNDA KAYI GULMARSA.. IN BA HAKA BA KUMA, TO KAJE KA NEMESHI YA YAFE MAKA".
Sai na farka a firgice, na tafi cikin Masallacin nan ina ta dubawa ko zan samu wannan mutumin. Nayi ta nemansa sai bayan kwana uku sannan na hadu dashi.
Yana kallona sai yace mun "Yanzu kai Junaidu, kamar kai, ka rika cin naman mutane!?."
Daga jin haka ban san lokacin da na suma ba.. Da na farfado na ganshi yana tare dani. Sai yace mun ''Shin zaka Qara?". Nace masa ''A'a". Sai yace "To Allah shi gafarta mana baki daya".
Shikenan sai ya tafi, tun daga ranar ban sake ganinsa ba...
(Shaikh Abdurrahman Ibnul Jawzee ne ya kawo wannan Qissar acikin littafinsa Uyunul Hikayaat).
BAYANI
********
Wannan labarin yana karantar damu abubuwa da yawa. Daga cikinsu akwai :
1. Muhimmancin kiyaye harshenka dake cikin bakinka, da kuma harshen zuciyarka daga cin naman mutane. Har ma da harshenka dake bisa yatsunka da kake yin rubutu dasu da alkalami ko rubutu a internet.
2. Allah yana da Salihan bayinsa wadanda ya boyesu acikin siffofi daban daban. Don haka kar ka raina mutum don ka ganshi acikin yagaggun tufafi, ko don bashi da komai.
3. Laifin da wani yayi aka kyaleshi, wani kuma idan yayi sai an nuna masa kuskurensa.
4. Ka rika amsa laifinka da neman yafewar kusakurenka komai kankantarsa.
Allah yasa mu dace. Ameeen.
Allah yasa daliban Zauren Fiqhu da dukkan sauran jama'a zamu dubi wannan madubi da kyau domin amfanar rayuwarmu. Ameeen.
31/03/2026
2023
KWANKWASO / ABBA
GANDUJE / GAWUNA
2027
KWANKWASO / GAWUNA
GANDUJE / ABBA
DARASI:- A RAYUWA BABU MAƘIYI NA DINDINDIN, BABU MASOYI NA DINDINDIN,
MAƘIYINKA A YAU ZAI IYA ZAMA MASOYINKA GOBE,
MASOYINKA A YAU ZAI IYA ZAMA MAƘIYINKA GOBE.
MUBI DUNIYA A HANKALI...
Click here to claim your Sponsored Listing.