N R HAUSA TV

N R HAUSA TV

Share

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labarai ingantattu waɗanda babu wai-wai. WhatsApp Number 08139283352.

01/07/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Senatorr Usman Forlife, Abdurrahim Umar Kura, B M Abdullahi Maitaya, Ameenerh Abdullah Ameenerh Abdullah

29/06/2025

An kaddamar da shugabancin ƙungiyar Minjibir/Ungogo Kwankwasiyya concern forum.

Kungiyar dai ta tsaida matsaya kan tabbatar da shugabanci na gari a Minjibir da Ungogo da kuma kawar da baragurbin shugabanni a yankin.

A zaman ƙungiyar na farko a zaɓi shugabancin rikon kwarya inda Abubakar Bachirawa ya kasance shugaban kungiyar.

Abba Kabir Yusuf
Hon. Sani Wakili
Kwankwasiyya Reporters
Rahama Sadau

29/06/2025

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Sakataren Jam’iyyar na Kasa, Mista Oginni Olaposi, ya fitar ranar Lahadi a Legas.

Olaposi ya mayar da martani ne kan murabus din da Abdullahi Ganduje ya yi daga shugabancin APC da kuma jita-jitar cewa ya yi hakan ne domin ba wa Kwankwaso damar shiga jam’iyyar.

“Kwankwaso ya ci amanar da muka ba shi ta hanyar kokarin kwace jam’iyyar daga hannun wanda ya kafa ta, Dokta Boniface Aniebonam, wanda ya ba shi damar samun tikitin takarar shugaban kasa kyauta a 2023,” in ji shi.

Photos from N R HAUSA TV's post 28/06/2025

Har yanzu al'ummar Gayawa Titin Badaru dake yankin karamar hukumar Ungogo na fama da matsalar zai-zayar ƙasa.

Abba Kabir Yusuf
Gandujiyya Online
Aminu Saira
Rahama Sadau

28/06/2025

‎Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa babu wani sauyi da aka samu a matsayin Sanata George Akume, wanda har yanzu ke ci gaba da zama Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF).

‎Wannan na zuwa ne bayan yaduwar jita-jita da ke cewa an sauke shi daga mukaminsa.

‎A cewar wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai ba Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu shawara na musamman kan harkokin yada labarai ya fitar a yau Asabar, Shugaban Ƙasa bai yi wani sabon naɗi ba dangane da mukamin SGF.

Abba Kabir Yusuf
Rahama Sadau
Aminu Saira
Gandujiyya Online

28/06/2025

Mai dakin shugaban kasa Mr. Remi Bola Ahmad Tinubu ta bada tallafin Naira miliyan 110 ga iyalan yan wasan jihar Kano 22 wadanda s**a rasu sakamakon hatsarin a hanyarsu ta dawowa gida bayan kammala gasar wasannin motsa jiki ta kasa.

Da take gabatar da tallafin ga iyalan mamatan, Mai dakin shugaban kasa Mrs. Remi Tinubu wadda ta samu wakilcin Mai dakin mataimakin shugaban majalisar dattijai Hajiya Laila Barau Jibril, ta bayyana alhininsa bisa rasuwar su.

28/06/2025

Waiwaye: ko me ƴan Nigeria zasu iya tunawa a wannan ranar?

28/06/2025

‎Ana neman tono gawar tsohon Gwamnan Jihar Oyo, Otunba Christopher Adebayo Alao-Akala, domin yin gwajin jini (DNA) da nufin tantance halastattun ’ya’yansa da za su ci gadon dukiyar da ya bari.

Me zaku ce?

28/06/2025

An shiga ruɗani bayan sace wata mashahuriyar Tukunya da ta kai kimanin shekaru 30 ana girki da ita.

Matashi Abdurrahim Umar Kura shi ne ya wallafa ɓacewar Tukunyar wanda ya ce sun girgiza da jin sace wannan Tukunya la'akari da yadda ɗanɗanan girkin ta daban yake da sauran Tukwane.

Zalika matasin ya bukaci duk wanda yaga wannan Tukunya tasu da ya taimaka ya tuntube su.

28/06/2025

Fagen wasanni: ‎A irin wannan ranr ta 28-06-2007 ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcalona ta ɗauki ɗan wasa Yaya Touré akan kuɗi €9M.

Want your business to be the top-listed Media Company in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Address


Kano